1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Girgizar kasa ta kashe mutane tara a Japan

Zainab Mohammed AbubakarApril 15, 2016

Jami'an agaji na cigaba da aikin ceton mutanen da suka makale a tsakanin dubban gidajen da suka ruguje, sakamakon mummunar girgizar kasar.

https://p.dw.com/p/1IWFn
Japan Erdbeben
Hoto: Getty Images/AFP/Jiji Press

A kalla mutane tara ne suka rasa rayukansu sakamakon wata mummunar girgizar kasa data ritsa da tsibirin Kyushu da ke kudancin kasar Japan a daren wannan Jumma'ar.

Rahotanni kafofin yada labarun kasar na nuni da cewar wasu mutane 760 suka jikkata, 44 daga cikinsu kuwa munana.

Sama da mutane 4000 da ke zaune a wannan tsibiri ne dai suka tsere daga gidajensu, saboda tsoron abun da zai iya biyo bayan girgizar kasar mai karfin maki 6.5.