1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ghana ta samu ci gaba ta fuskar arzikin zinare

June 8, 2024

Hukumomin kasar Ghana sun bayyana cewa kasar ta samu karuwar arziki a fannin ma'adinin zinare da ake hakowa. Kasar ta samu karuwar ne bayan sauya dabaru a harkar ma'adinanta.

https://p.dw.com/p/4gp9I
Shugaba Nana Addo Dankwa Akufo-Addo na kasar Ghana
Shugaban Ghana, Nana Addo Dankwa Akufo-AddoHoto: Getty Images/S. Gallup

Rahotannin da ke fitowa daga kasar Ghana, na nuna cewa kasar na samun ci gaba da fuskar arzikin Gwal wato Zinare, inda alkaluma ke nuna cewa ta samu karuwa da kashi 8.3% .

Hakan na nufin a shekarar da ta gabata Ghanar ta samu karin nauyin Zinare miliyan hudu, daga abin da hukumar kula da harkokin hakar albarkatun karkashin kasa ta nunar a jiya Juma'a.

Ci gaban da kasar ta Ghana ta samu a fannin ma'adinin dai, na da alaka ne sosai da abin da matsaikatan masu aikin hako zinaren suka yi.

Ana dai hasashen kasar ta iya samun karuwa a bana da akalla zinare mai nauyin miliyan 4.5 a ma'aunin ounce.