Fafatawa tsakanin Jamus da Yurugai
July 10, 2010A cigaba da gasar cin kofin ƙwallo ta duniya da ake gwabzawa a ƙasar Afrika ta Kudu, a wannan Asabar ake fafatawa tsakanin Jamus da Yurugai domin tantance ƙasar da za ta maye gurbi na ukku. Tashar rediyon DW za ta watsawa kai tsaye wannan wasa da zai wakana a filin ƙwallon Port Elizabeth.
A yayin da ya ke bayyani akai shaharraren ɗan wasan nan na Jamus Thomas Müller cewa yayi:
"Ina kyautata zaton a wannan karo Ƙungiyar ƙwallon ƙafar Jamus za ta buga wasa na ƙwarai. Hakan ya zama wajibi gare mu ta yadda za mu kammala wasan cikin nasara".
Gobe idan Allah ya kai mu, Spain za ta buga wasan ƙarshen da Holland.
A cen ƙasar ta Holland, gwamnatin ta ɗauki dokar hana shan barasa a wuraren da aka keɓewa jama´a domin kallan gasar. Gwamnatin ta yi hakan da zumar yin rigakafi ga abkuwar haɗarrurruka.
Mawwallafi: Yahouza Sadissou Madobi
Edita: Mohamed Nasiru Awal