Fifa ta yi barazana dakatar da Nageriya
July 2, 2010Hukumar wassannin ƙwallon ƙafa ta duniya wato Fifa ta yi barazana dakatar da ƙasar Nageriya daga wasannin ƙwallon ƙafa na ƙasa da ƙasa , idan har gwamnatin ƙasar bata dawo akan matakin da ta ɗauka na janye ƙungiyar yan wassan Super Eagles ba daga fagen wasannin na tsawon shekara biyu kafin nan da ranar litinin.
Hukumcin dakatarwa dai da ƙungiyar ta FIFA zata ɗauka akan Nageriya ya haɗa da soke kuɗaɗen tallafin da hukumar ke baiwa ƙasar da dakatar da ƙungiyar wassannin ta ƙasar sanan kuma da haramtawa duk wani alƙalin wasannin ƙwallon ƙafa na Nageriya aikin alƙalancin gasar ƙasa da ƙasa ta ƙwallon ƙafa.
yanzu haka dai hukumar ta FIFA ta sanar da cewa zata tura wani wakilin ta a ranar litinin mai zuwa a ƙasar ta Nageriya domin tattaunawa da hukumomin akan wannan badaƙala da ta kuno kai.
Mawallafi Abdourahamane Hassane
Edita Halima balaraba Abas