1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Charles Michel: Bukatar sake kintsa Turai bayan Corona

Abdoulaye Mamane Amadou
April 22, 2020

Shugaban hukumar tarayyar Turai Charles Michel, ya ce akwai bukatar sake farfado da nahiyar da hada karfi da karfe don sake inganta EU idan har aka kawo karshen masifar annobar Covid-19.

https://p.dw.com/p/3bFC4
Belgien | Pressekonferenz Ursula von der Leyen und Charles Michel nach Treffen mit Erdogan
Hoto: Reuters/F. Lenoir

Shugaba Charles Michel na jawabin ne a yayin wata gayyatar da ya yiwa shugabannin kasashe membobi a kungiyar zuwa wani taron koli ta hanyar na'urar sadarwa ta bidiyo a gobe Alhamis. Michel ya ce annobar Corona ta nuna wa kasashen karara irin muhimmancin da ke da akwai na sarrafa abubwan da ake da  tsananin bukatarsu a cikin nahiyar, karfafa wa kamfanoni da masana'antun cikin gida domin rage dogaro da wasu da ke waje.

Kalaman shugaban na zuwa ne a yayin da wasu daga cikin kasashen Turan suka fara sassauta dokokin kulle duk da barnar da cutar Corona ta yi mafi muni ga wasu kasashen kungiyar.