1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Faransa za ta karfafa yaki da ta'addanci

Mohammad Nasiru AwalApril 29, 2015

A sakamakon jerin hare-hare da ta fuskanta a birnin Paris a watannin baya, Faransa za ta kara kasafin kudin yaki da barazanar ta'addanci.

https://p.dw.com/p/1FHoT
Frankreich Präsident Francois Hollande Sitzung Verteidigungsrat
Hoto: Reuters/G. Fuentes

Gwamnatin Faransa ta ba da sanawar karfafa aikin sojojin ta a wani mataki na dakile barazanar da take fuskanta daga 'yan ta'adda a ciki da wajen kasar. Shugaban Faransa Francois Hollande ya ce a cikin shekaru hudu masu zuwa farawa daga shekarar 2016, za a yi wa ma'aikatar tsaron kasar karin kasafi na Euro miliyan dubu 3.8. Bugu da kari shugaban ya yanke kudurin girke karin sojoji 7000 don yaki da ta'addanci a cikin gida. Tun bayan jerin hare-haren da aka kai a birnin Paris a cikin watan Janeru, Faransar ta kara tsaurara matakan tsaro da yawan dakarun sintiri a fadin kasar baki daya.