Maroko ta yi rawar gani a Qatar
December 15, 2022Talla
Faransa ta taka wa Maroko birki ga zuwa zagayen karshe na cin kofin duniya na kwallon kafa da ake yi a Qatar bayan da ta doketa da ci biyu da nema . A yanzu Faransa za ta kara da Ajantina a karawar ta karshe da za a yi ranar Lahadi, Daman dai Faransa ce ke rike da kofin da ta yi nasara a gaban kureshiya a gasar duniyar da aka yi a rashar a 2018.A Karawa ta karshe da Faransa ta yi da Ajantina a shekara 2018 Faransar ta samu nasara a ci hudu da uku