1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Faransa ta kama mutuman da ya kai hari Lyon

Gazali Abdou Tasawa
May 27, 2019

'Yan sanda a Faransa sun kama wani matashi dan asalin Aljeriya da ake zargi da kai harin ta'addanci da bam kirar gargajiya a birnin Lyon a ranar Juama'ar da ta gabata.

https://p.dw.com/p/3JCUW
Frankreich Lyon Polizist bei Spurensicherung nach Bombenanschlag
Hoto: Reuters/E. Foudrot

Hukumomin shari'a a kasar Faransa sun sanar da kame wani matashi dan asali kasar Aljeriya mai shekaru 24 wanda ake zargi da kasancewa mutuman da ya dana bam kirar gargajiya da ya jikkata mutane 13 a birnin Lyon a ranar Juma'ar da ta gabata. 

Kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP ya ruwaito magajin garin birnin na Lyon Gerard Collomb na cewa maharin dalibi ne da ke karatun a makarantar koyar da ilimin konfuta da amma ba ya a cikin rijistan masu aikata laifuka na 'yan sanda. 

Hukumomin shari'a sun kuma sanar da kama mahaifiyar maharin da wani dalibi dan makarantar sakandare dan asalin kasar Aljeriya da ke da kusanci da maharin.