1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

ICC za ta binciki zargin laifukan yaki a Falasdinu

Lateefa Mustapha Ja'afarJune 26, 2015

Ministan harkokin kasashen ketare na Falasdinu Riad Malki ya mika wani kundi ga kotun hukunta masu aikata manyan laifukan yaki ta kasa da kasa wato ICC.

https://p.dw.com/p/1Fnfk
Riad al-Malki ministan harkokin kasashen ketare na Falasdinu
Riad al-Malki ministan harkokin kasashen ketare na FalasdinuHoto: Reuters

Kundin dai na kunshe ne da shaidun da zasu tabbatar da zargin kisan kiyashi da suke yiwa Isra'ila a farmakin da ta ke kaiwa a yankin Zirin Gaza da kuma Gabar Yamma da Kogin Jodan. A yanzu haka dai mai gabatar da kara ta kotun Fatou Bensouda za ta fara gudanar da binciken sharar fage domin tabbatar da zargin Isra'ila da aikata laifukan yaki a Falasdinun. Matakin na zuwa ne kwana guda bayan da wani bincike da Majalisar Dinkin Duniya ta gudanar ya zargi Isra'ila da Falasdinu da yiwuwar aikata laifukan yaki a yayin yakin da suka gwabza da juna a yankin Zirin Gaza a shekarar da ta gabata ta 2014. Tuni dai Isra'ilan ta yi watsi da wannan batu tana mai cewa ita ba mamba ba ce a kotun ta ICC.