Shugabannin Turai za su tabka mahawara a kai
June 21, 2018Talla
Sai dai ta jaddada cewar, ba ta da niyar samar da wuri makamancin sansanin gwale gwale na Guantanamo ga 'yan gudun hijirar. Hukumar gudanarwa ta EU ta ce cikin tsarin, an sanya dukkan matakai na kariya ga 'yan gudun hijirar da aka ceto daga cikin Teku a kan hanyarsu ta zuwa Turai.
A mako mai zuwa nedai ake saran mahawara kan wannan batu a taron Kungiyar Tarayyar Turai da zai gudana a birnin Brussels din kasar Beljium.
Amurka ta fuskanci fushin kasashen duniya lokacin da ta fara amfani da sansanin sojin ruwanta da ke Guantanamo a kasar Kuba, wajen azabtar da wadanda take zargi da ta'addanci, tun bayan hare haren 11 ga watan Satumban 2011 a kasar.