1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Al'ummar Tigray na kada kuri'unsu

Zainab Mohammed Abubakar
September 9, 2020

A wannan Larabar ce al'ummar yankin Tigray da ke arewacin Ethiopiya ke kada kuri'unsu, a zaben da ke zama nuna turjiya ga umurnin framinista Abiy Ahmed.

https://p.dw.com/p/3iDut
Äthiopien Region Tigray Wahlen
Hoto: DW

Fraiministan ya ayyanashi a matsayin saba doka, duk da cewar gwamnati ba ta da niyyar martani da jami'an tsaro.

A baya dai an tsara gudanar da zaben yankunan kasar ta Ethiopiya a ranar 29 ga watan Augustan da ya gabata, kafin a dage shi saboda barkewar annobar corona. 'Yan adawa a yankin na Tigray sun zargi Abiy Ahmed da kokarin fadada wa'adinsa na mulki. 

Sa-in-sa da Tigray, na daga cikin rigingimun baya-bayannan da fraministan Ethiopiyan ke fuskanta, mutumin da ke fafutukar dinke barakar da ke barazanar wargaza hadin kan kabilun kasar sama da 80.

Tuni dai 'yan siyasar Tigray suka yi gargadin cewar, yunkurin tsayar da kuri'un da aka fara kadawa a zaben na yau, zai fuskanci martanin yaki.