1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

ECOWAS za ta yi taro kan Nijar

Abdourahamane Hassane
July 28, 2023

Shugabannin kasashen yankin yammacin Afirka za su yi taro a Abuja ranar Lahadi bayan juyin mulkin da sojoji suka yi, wanda ya hambarar da zababben shugaban kasar Nijar Mohamed Bazoum.

https://p.dw.com/p/4UWfw
Nigeria | ECOWAS Gipfel
Hoto: Präsidentschaft von Niger

Fadar shugaban Najeriya wanda shi ne ke jagorantar kungiyar ta  ECOWAS ita ce ta sanar da haka. Kungiyar ta ECOWAS ta na shirin daukar mataki a kan nijar din. A karon farko tun bayan juyin mulkin da ya yi sabon jagoran mulkin sojin na Nijar Janar Abdourahamane Tchiani ya yi jawabi a gidan telbijan da rediyo na kasar inda ya bayyana dalilansu na yin juyin mulki.