1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Duniya na Allah wadarai da abinda ya faru a Amirka

Abdoulaye Mamane Amadou
January 7, 2021

Rikicin siyasar Amirka na jan hankalin kasashen duniya, lamarin da yasa shugabannin kasashen duniya ke tsokaci kan rashin amincewa da sakamakon zabe da Shugaba Donald Trump ya yi.

https://p.dw.com/p/3ndbF
USA Washington | Sturm auf das Kapitol
Hoto: Manuel Balce Ceneta/AP Photo/picture alliance

Kasashen China da Rasha da Iran da dama ke takun saka da gwamnatin shugaba Donald Trump, a cikin wani yanayin zumde sun yi bayyana abin da ke faruwa a Amirka a matsayin raunin dimukuradiyya.

Babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres, ya bayyana kaduwa tare da fatan ganin kasar ta dawo hayyacinta, a yayin Shugaba Emmaneul Macron na Faransa, ya yi kakkausar suka ga matakin na magoya bayan Donald Trump, yana mai cewa " Ba za mu bari wasu kwarorin masu tayar da zaune tsaye su mayar da hannun agogon ci gaban dimukuradiyya baya ba".

Haka suma sauran shuwagabannin a kasashen Isra'ila da Kanada da Austriya da Holand da Spain da Nerland, duk sun yi kakkausar suka kan matakin.

Shugaban Jamus Frank-Walter Steinmeie a wani sakon bidiyiyonsa, ya bayyana kaduwa da abinda ya faru a harabar majalisar dokokin ta Amirka. "Ya ce Bacin rai da kyama na saka dimukuradiyya cikin hadari, haka kuma karya da tashe-tashen hankula na kasancewa babban hadari ga tsarin dimukuradiyya."