1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kasashe na tayin kai wa Turkiyya agaji

Abdullahi Tanko Bala
February 6, 2023

Shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya ce kawo yanzu kasashe kimanin 45 sun yi tayin bai wa kasar taimakon jinkai bayan Iftila'in girgizar girgizar kasa da ta afkawa kasar a wannan litinin

https://p.dw.com/p/4N98b
Türkei | Erdbeben Diyarbakir
Hoto: IHA agency via AP/picture alliance

A jawabin da ya yi da aka yada ta akwatunan talabijin, Erdogan ya ce adadin mutanen da suka rasu sun kai mutum 912 yayin da wasu 5,400 kuma suka jikkata. An kuma ceto mutane 2,470 daga baraguzan gine-gine.

Gidaje kimanin 3,000 suka ruguje a girgizar kasar. Baki daya mutanen da suka rasu a girgizar kasar a Turkiyya da Syria sun haura mutum 1, 400

Sakataren kungiyar kawancen tsaro ta NATO Jens Stoltenberg ya ce mambobin kawancen kungiyar suna gangami domin taimaka wa Turkiyya tunkarar kalubalen iftila'in.

Rasha ta ce za ta tura ma'aikatan ceto zuwa Turkiyya domin taimaka wa Turkiyyar da makwabciyarta kasar Syria.