Dakarun Siriya sun sake kutsawa birnin Hama
July 31, 2011Rahotanni daga Siriya na nuni da cewar da sanyin safiyar yau ne Tankokin soji sun kutsa birnin Hama, bayan mamayar da suka yi na sama da wata guda sakamakon zanga-zangar adawa mafi girma da al'ummomin yankin ke gudanarwa. Wani likita mazaunin garin na Hama wanda yaƙi a faɗi sunansa, ya shaidar da cewar kutsen sojin ya kashe a kalla mutane 17 har da wani matashi mai suna Fares al-Naem. Ya ce sojojin gwamnatin na Siriya na kai hare-hare daga kusurwowi huɗu na garin, da manyan makamai. Shugaba Bashar al-Assad dai ya kokarin dakatar da zanga-zangar adawa da mulkinsa na shekaru 11, wanda ya ɓarke tun a watan Maris, sakamakon boren neman sauyi daya faro daga ƙasashen Masar da Tunisiya wanda kuma ke cigaba da gudana a ƙasashen larabawan.Tuni dai hukumomin Siriya suka kori 'yan jaridar ketare daga ƙasar, batu dake kawo cikas a dangane da sahihancin rahotanni da ake samu daga wannan ƙasa.
Mawallafiya: Zainab Mohammed Abubakar
Edita : Abdullahi Tanko Bala