1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Dakarun kasa da kasa a Somaliya

September 28, 2012

Sojojin kasar Kenya ne suka kutsa a garin Kishmayo da nufin zakulo mayakan kungiyar kishin islaman Al-shebab a Somaliya.

https://p.dw.com/p/16H3I
FILE - In this Monday, Feb. 20, 2012 file photo, Kenyan army soldiers stand in a dugout position at their base in Tabda, inside Somalia. Kenya's military said Friday, Sept. 28, 2012 that its troops attacked Kismayo, the last remaining port city held by al-Qaida-linked al-Shabab insurgents in Somalia, during an overnight attack involving a beach landing. (AP Photo/Ben Curtis, File)
Hoto: dapd

Sojojin kasar Kenya da ke cikin rundunar gamayar Afrika da ke kasar Somaliya,sun aukawa garin Kishmayo garin da ke matsayin sansanin mayakan kungiyar kishinn islama ta Al-shebab a wannan juma'ar. A lokacin da ya ke wa manema labarai bayani,kakakin rundunar tsaron kasar Kenya kanar Cyrus Oguna ya ce sojojin Kenya sun samu nasarar kwace garin daga hannun mayakan ba tare da sun fusdkaci wata mumunar turjiya ba. To saidai wani mai magana da yayun kungiyar ta Al-shebab Chekh Abdulaziz Abu Musab ya musanta kama garin inda ya ce lallai an samu wasu sojojin kasar ta Kenya da suka yi yukunrin shiga to saidai mayanknsu suka mayarda su baya.
Birnin na Kishmayo shi ne gari mafi girma a kudancin kasar inda masu kishin islaman ke samun kudaden shiga a dangane da hada-hadan kasuwancin gabar tekun yankin.

Mawallafi: Issoufou Mamane
Edita: Mouhamadou Awal Balarabe