1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Dakarun gwamnatin Iraƙi sun ƙwace iko da garin Baiji

Abdourahamane HassaneNovember 14, 2014

Dakarun sun karɓe iko da garin mai matatar man fetir mafi girma da ke a yankin arewacinn kasar bayan sun kwashe kusan makonnin huɗu suna gwabza ƙazamin fada da Ƙungiyar IS.

https://p.dw.com/p/1DnsK
Irak Kämpfe bei der Raffinerie von Baidschi 31.07.2014
Hoto: picture-alliance/dpa

Masu aiko da rahotannin sun ce sake karɓe iko da birni na Baiji da ke a arewacin bagadaza. Zai ƙara ƙwarin gwiwa wa dakarun gwamnatin wajen ƙarfafa tsaro a kan matatar man fetir ɗin da mayaƙan IS suka ƙwace a cikin watan Yunin da ya gabata.

Wannan yunƙurin dai na sojojin gwamnatin na iraki na zaman wata babbar nasara da suka samu a kan masu jihadin tun lokacin da aka fara yin faɗan.