1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaban Afirka ta Kudu ya sha ihu

Lateefa Mustapha Ja'afar
December 16, 2022

Masu zanga-zanga sun kawo tarnaki, a yayin da shugaban kasar Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa ke jawabin bude babban taron jam'iyyarsa mai mulki ta ANC da zai ba su damar zabar sababbin shugabannin jam'iyyar.

https://p.dw.com/p/4L57w
Afirka ta Kudu | Siyasa | ANC | Kalubale | Cyril Ramaphosa | Adawa
Har yanzu akwai sauran aiki gaban shugaban Afirka ta Kudu Cyril RamaphosaHoto: Themba Hadebe/AP/dpa/picture alliance

Masu zanga-zangar da ke ihun "dole Ramaphosa ya tafi", sun tilasta Shugaba Cyril Ramaphosa yin magana da karfi domin a ji abin da yake fada a jawabin nasa. Wakilan jam'iyyar ta ANC daga sassa dabam-dabam na kasar, na yin taro domin zabar sabon shugaba da ma wanda zai tsaya mata takarar shugaban kasa a zabe na gaba da za a gudanar a shekara ta 2024 a kasar. Shi dai Shugaba Ramaphosa na fatan yin tazarce a mastsayin shugaban jam'iyyar ta ANC da ta kwashe shekaru 28 tana shugabanci a Afirka ta Kudu, duk da zubewar da mutumcinsa ya yi sakamakon zargin almundahana da ma farin jinin jam'iyyar da ke raguwa.