1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Cutar kyandar biri ta bulla a karon farko a Ghana

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim MAB
October 4, 2024

Daga watan Janairu zuwa yanzu, fiye da mutane 860 cutar ta kyandar biri ta halaka a nahiyar Afirka ciki har da Ghana, bayan da ta kama mutane 34,297, in ji hukumar CDC mai yaki da yaduwar cututtuka ta Afirka.

https://p.dw.com/p/4lOND
Yara sun fi kamuwa da cutar kyandar biri a kasashen Afirka
Yara sun fi kamuwa da cutar kyandar biri a kasashen AfirkaHoto: Ruth Alonga/DW

Ghana ta tabbatar da bullar cutar kyandar biri a karon farko a kasar, bayan da ta kama wani yaro a yankin Yamma maso arewacin kasar, a daidai lokacin da take ci gaba da yaduwa a nahiyar Afirka. Babban daraktan hukumar lafiya ta kasar Patrick Kuma-Aboagye, ya ce tuni suka killace yaron bayan da nuna alamun kamuwa da cutar, wato zazzabi da ciwon gabobobi, inda suke gudanar da bincike a kan mutane 25 da suka kusance shi, don tabbatar da sanin ya ya koshin lafiyarsu yake.

 

Karin bayani:Kwango na maraba da tallafin rigakafin Mpox

Babban jami'in na Ghana ya kara da cewa akwai rahotannin mutane 230 da suke gudanar da gwaje-gwaje a kansu, don kauce wa yaduwar cutar mai saurin kisa.Daga watan Janairu zuwa yanzu, fiye da mutane 860 cutar ta kyandar biri ta halaka a nahiyar Afirka, bayan da ta kama mutane 34,297, kamar yadda shugaban hukumar dakile yaduwar cututtuka ta Afirka CDC Jean Kaseya ya sanar jiya Alhamis.