1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Corona ta sake yaduwa a Turai

Abdourahamane Hassane
March 22, 2022

Hukumar Lafiya ta Duniya OMS Ko WHO ta ce cutar corona ta sake karuwa a cikin wasu ksashen Turai wadanda suka yi gagawa soke matakan rigakafi na yaki da annobar.

https://p.dw.com/p/48qQT
Deutschland Coronavirus Symbolbild Hinweisschild Omikron Subtyp BA.2
Hoto: Torsten Sukrow/SULUPRESS.DE/picture alliance

Darektan hukumar lafiyar Reshen Turai Hans Kluge ya ce coronar ta sake yaduwa a karkashin nau'in BA2 a Jamus da Birtaniya da Faransa da Italiya da cikin wasu kasashen guda 18 na Turai. Hukumar Lafiyar ta Duniya WHO ta ce a  cikin kwanaki bakwai da suka gabata, an sami sabbin mutane sama da miliyan biyar  da suka kamu da cutar, yayin da wasu sama da dubu 12 suka mutu a Turai.