1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ci gaba da shari'ar tsohon shugaban Masar

August 15, 2011

Kotu ta sanya 5 ga watan Satumba a matsayin ranar ci gaba da sauraren shari'ar tsohon shugaban Masar da wani tsohon minista a gwamnatin sa

https://p.dw.com/p/12Gqk
Hosni Mubarak, kwance a gadon asibiti kuma a cikin wani keji yayin zaman kotuHoto: Egyptian State TV/dapd

Kotun dake sauraren shari'ar tsohon shugaban ƙasar Masar Hosni Mubarak ta ɗage ci gaba da shari'ar har ya zuwa ranar biyar ga watan Satumba. Tsohon shugaban, mai shekaru 83 a duniya, ya yi bayyanar sa ta biyu a cikin kotu kwance akan gadon asibiti.

Alƙalin da ke sauraren shari'ar, wadda ta haɗa da 'ya'yan tsohon shugaban su biyu, ya faɗaɗa tuhumar ta ƙunshi tsohon ministan kula da harkokin cikin gidan ƙasar ta Masar Habib el-Adly. Hakanan kuma alƙalin ya ce daga yanzu ba za'a ci gaba da nuna shari'ar - kai tsaye ta na'urorin telebijin ba.

Ana dai tuhumar tsohon shugaban na Masar ne da hannu wajen kissar masu boren adawa da gwamnati yayin zanga-zangar adawar da ta kifar da gwamnatin nasa a tsakanin watan Janairu da kuma Fabrairun bana. Tuni dama tsohon shugaban ya yi watsi da zarge-zargen.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh

Edita : Abdullahi Tanko Bala