1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

China: Masu zama a Amirka su yi taka tsan-tsan

Abdoulaye Mamane Amadou
June 4, 2019

Ma'aikatar yawon shakatawa da bude idanu ta kasar China, ta shawarci 'yan kasar da su bude ido kan duk inda za su sanya kafa a kasar Amirka duba da tsamin danganta da ke tsananin kasashen biyu.

https://p.dw.com/p/3Jphs
Symbolbild USA-China-Handelskrieg
Hoto: Colourbox

Shugabannin kasar China sun koka da rashin tabbataccen tsaro da cin zarafi ga 'yan kasar idan suka je a Amirka. Wannan gargadin na kasar China ga 'yan kasarta, na zuwa ne a daidai lokacin da tsamin dangantaka da takaddama ke kara zafafa tsakanin gwamnatin Washington da Pekin kan batun cinikayya, musamman ma matakin baya-bayan nan da gwamnatin Donald Trump ta dauka kan kamfanonin China ciki har da kamfanin kera wayar salula na Huawei.