1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Chamisa: Zan kalubalanci zaben Zimbabuwe

Mouhamadou Awal Balarabe
August 2, 2018

Shugaba Mnangagwa na Zimbabuwe da madugun 'yan adawa Chamisa na ci gaba da ikirarin lashe zaben shugaban kasar Zimbabuwe duk da cewa ba a bayyana sakamakon zabe ba.

https://p.dw.com/p/32YEo
Nelson Chamisa
Hoto: DW/P. Musvanhiri

Manyan 'yan takara a zaben shugaban Kasar Zimbabwe na ci gaba da ikirarin samun nasara a zaben da ya gudanar ranar Litinin, a daidai lokacin da ake ci-gaba da dakon cikakken sakamakon daga hukumar zabe mai zaman kanta. Masu sa ido na kasa da kasa sun bukaci hukumar zaben da ta hanzarta sanar da sakamakon don kauce wa tashin hankali bayan kashe mutane shida a ranar Laraba a wani rikici tsakanin jami'an tsaro da magoya bayan 'yan adawa.

Madugun 'yan adawa Nelson Chamisa ya bayyana cewa shugaba mai ci a yanzu Emmerson Mnangagwa ya rigaya ya san ya fadi zabe, saboda haka zai kalubalanci sakamakon zabe idan aka samu akasi. Amma kuma jam'iyyar ZANU-PF da ke mulki ta ce dan takararta na kan samun nasara.

Sojoji sun killace manyan titunan birnin Harare duk da kira da kasashen waje da kungiyoyin duniya suka yi na a kwantar da hankali don da ka da a jefa kasar cikin rikicin siyasa.