Sabon harin Boko Haram a Chadi
March 22, 2019Talla
Sojoji 23 aka kashe a yankin Kudu maso Yammacin kasar Chadi a wannan Juma'ar, a wani hari da mayakan Boko Haram suka kai musu, a cewar majiyar dakarun a birnin N'Djamena.
A ta bakin jami'in sojin kasar, mayakan na Boko Haram sun afkawa sansanin dakarun na Chadi da misalin karfe daya na dare, inda suka kashe 23 daga cikinsu.