1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Burkina ta nemi Faransa ta janye jakadanta

January 4, 2023

Matakin na zuwa ne kasa da makonni biyu bayan da sojojin na Burkina Faso suka bukaci babbar jami'ar MDD da ke kula da ayyukan agaji Barbara Manzi da ta bar kasar bayan da suka zarge ta da kambama halin rashin tsaro.

https://p.dw.com/p/4LiKL
Shugaban mulkin sojan Burkina Faso Kyaftain Ibrahim TraoreHoto: Kilaye Bationo/AP Photo/picture alliance

Gwamnatin mulkin soji ta Burkina Faso ta bukaci Faransa ta janye jakadanta Luc Hallade daga kasar, a daidai lokacin da kin jinin Faransa ke ci gaba da bazuwa a kasar da ke Afirka ta Yamma wacce ke kokarin kara karfin dangantaka da kasar Rasha.

Mai magana da yawun gwamnatin Burkina Faso Jean-Emmanuel Ouedraogo  ya tabbatar wa da kamfanin dillancin labarai na  Associated Press wannan mataki. Sai dai ya kauce wa yin karin bayani a kan lamarin.

Ofishin jakadancin Faransa da ke Ouagadougou ya ce ya samu kwafin takardar da aka aike masa da wannan bukata amma bai yi wani karin haske ba.