1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Burkina Faso za ta tattauna da 'yan ta'adda

April 2, 2022

Sojojin Burkina Faso sun ce za su gano tare da tattaunawa da 'ya'yan kungiyoyin da suka hana Burkina Faso zaman lafiya domin a dinke barakar da ke faruwa, a dawo da zaman lafiya a kasar da ke Afirka ta Yamma.

https://p.dw.com/p/49Nic
Burkina Faso | Militärleiter Paul-Henri Sandaogo Damiba
Hoto: Radiodiffusion TÈlÈvision du Burkina/AFP

Gwamnatin mulkin soji ta Burkina Faso ta kafa kwamitin da zai tattauna yiwuwar sulhu da mayakan jihadi da suka jima suna kai hare-hare a kasar. Laftanar Janar Paul-Henri Sandaogo Damiba, shugaban sojojin da suka kwace mulki a watan Janairu, ya fadi haka ne a yayin jawabin da ya yi wa 'yan kasar a birnin Ouagadougou a yammacin ranar Jumma'a.

A lokacin da sojojin kasar suka hambarar da gwamnatin tsohon shugaban kasa Roch Marc Kabore, sun ce kamarin da hare-haren mayaka masu ikirarin jihadi ke yi ne ya tilasta su kifar da gwamnatin ta dimukurdiyya. Sai dai watanni kusan uku da karbewar, matsalar na ci gaba da ruruwa.