1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Bunƙasa dangantaka tsakanin Jamus da Masar

April 19, 2011

Jamus ta ɗauki matakan taimakawa ƙasar Masar a ƙoƙarin ta na komawa bisa tafarkin dimoƙraɗiyya

https://p.dw.com/p/10vxN
Guido Westerwelle da Mohammed Tantawi, shugaban majalisar mulkin sojin MasarHoto: picture alliance/dpa

Ministan kula da harkokin wajen Jamus Guido Westerwelle ya isa birnin al-Qahira na Masar domin tattauna batutuwan da suka shafi siyasa tare da jami'an ƙasar, watanni tara kenan bayan masu rajin tabbatar da dimokraɗiyya a ƙasar suka tilastawa shugaba Hosni Mubarak yin murabus. Gwamnatin Jamus dai tana bayar da tallafin kuɗin daya kai Euro miliyan 50 a duk shekara ga ƙasashe irin su Masar da Tunisia domin taimaka musu bunƙasa sha'anin dimoƙraɗiyya ta hanyar gurabun ƙara ilimi da kuma shirye-shiryen baiwa 'yan ƙasar horo a fannonin ayyukan su.

A lokacin ziyarar dai, Guido Westerwelle zai gana tare da wakilan majalisar wucin gadin da ke gudanar da harkokin mulki a ƙasar ta Masar da kuma majalisar kula da haƙƙin bil'adama a ƙasar. Tunda farko ministan harkokin wajen na Jamus Guido Westerwelle ya bayyana cewar Masar za ta taka muhimmiyar rawa akan batun ko zanga-zangar neman sauye-sauyen dake gudana a ƙasashen larabawa daban daban za su kasance tubalin girka tsarin dimoƙraɗiyya mai ɗorewa a yankin.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh

Edita : Usman Shehu Usman