1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nazarin barin 'yan kallo shiga filin wasanni

Zainab Mohammed Abubakar
August 4, 2020

Manyan rukunin kungiyoyin kwallon kafa guda biyu na Jamus, na nazarin yiwuwar bai wa mutane damar shiga kallon wasannin Bundesliga a watan Satumba, bisa wasu sharudda saboda annobar corona.

https://p.dw.com/p/3gQ1q
Deutschland Christian Seifert beim DFL-Neujahrsempfang in Frankfurt
Hoto: picture-alliance/dpa/A. Dedert

A karkashin tsarin da hukumar wasanni ta tarayyar Jamus ta gabatar a kakar wasanni da za a fara a ranar 18 ga watan Satumba, kungiyoyin sun amince da muhimman batutuwa guda hudu.

Shugaban hukumar Christian Seifert ya ce, yiwuwar barin 'yan kallon zai ta'allaka ne da hukuncin da gwamnati za ta yanke, kuma a shirye suke na amincewa da matakan kamar yadda ya faru a baya.

" A yanzu ba cikar fili da 'yan kallo ne ke da muhimmanci a Jamus ba. Za a cigaba da mayar da fifiko kan lafiyar al'umma, kuma bai dace mu sake shiga wani hadarin idan har zamu iya kauce masa ba. A lokaci guda kuma ba zamu nade hannuwanmu ba tare da daukar wani mataki ba".