1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Boko Haram Ta yi barazanar afkawa Jami'ar Maiduguri

July 11, 2011

An fara bada shawarwari game da hanyoyin da ya kamata a bi domin warware taƙaddamar da ke tsakanin Boko Haram da kuma Gwamantin Tarayya

https://p.dw.com/p/11tI7

Hukumar kare hakkin bil adama ta tarayyar Najeriya ta bayyana cewar ta kaddamar da bincike kan zarge-zargen kisan ba gaira da aka yi wa shugabannin ƙungiyar Boko Haran shekaru biyun da suka gabata. Ita dai wannan hukumar ta ce ta yi wannan yunkuri ne dai domin a kauce wa fito na fito tsakanin gwamnati da 'yan boko haram da ya kai ga hallaka mutane da dama a garin maiduguri, tare da rufe jami'ar birnin daga wannan talatar.

A hannu guda kuma ƙungiyoyi masu zaman kansu na tarayyar ta Najeriya sun fara bayar da shawarwari game da hanyoyin da ya kamata a bi domin warware taƙaddamar da ke tsakanin Boko Haram da kuma gwamantin tarayya. Wannan mataki na su ya biyo bayan ruɓanya hare-hare akan bayin Allah da ba su ji ba su gani ba da ƙungiyar ta Boko Haram ta yi a ƙarshen mako a wasu Garuruwa na arewacin Najeriya ciki kuwa har da Kaduna.Daga Najeriyar wakilammu na Abuja Ubale Musa da Kaduna Ibrahima Yakubusuka aiko mana da karin bayani.

Mawallafiya: Zainab Mohammed Abubakar
Edita : Umaru Aliyu