1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Boko Haram ta hallaka mutane 7 a Diffa

Abdullahi Tanko Bala
November 23, 2018

Bayan samun zaman lafiya na wani dan lokaci 'yan Boko Haram sun kashe akalla mutane bakwai a wani hari da suka kai kauyen Toumour a jihar Diffa ta Jamhuriyar Nijar.

https://p.dw.com/p/38lni
Niger Flüchtlinge aus Nigeria
Hoto: DW/A. Cascais

A Jihar Diffa da ke Jamhuriyar Nijar, ma'aikata kimanin bakwai ne na wani kamfanin hakar ma'adanai tare da wani jami'in gwamnati suka rasa rayukansu a wani hari da 'yan Boko Haram suka kai lokacin da suke barci a gida.

Harin dai ya haifar da fadamuwa a yankin Diffa da ke makwabtaka da tafkin Chadi bayan samun kwanciyar hankali na dan wani lokaci. 

Dukkan mutanen da lamarin ya shafa 'yan Nijar. An kuma harbe su ne a kauyen Toumour da ke iyaka da Najeriya inda suke aikin haka rijiya domin samar da ruwa don inganta rayuwar 'yan gudun hijira da ke zaune a yankin.

Ma'aikatan suna aiki ne da kamfanin Foraco na kasar Faransa wanda ke aikin hakar ma'adanai da kuma rijiyoyin burtsatse.

Wasu mutane biyar sun sami munanan raunuka a kuma garzaya da su asibitin Diffa domin samun magani.

Rahotanni sun ce maharan sun yi awon gaba da motocin kamfanin guda biyu.