1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Boko Haram babban ƙalubale ga Najeriya

June 25, 2012

A karon farko shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ya amince da girman ƙalubalen Boko Haram dake gabansa a ƙoƙarin murƙushe ƙungiyar.

https://p.dw.com/p/15L4N
epa03046191 (FILE) A file photograph Goodluck Ebele Jonathan, President and Commander-in-Chief of the Armed Forces of the Federal Republic of Nigeria speaks during the general debate at the 66th session of the United Nations General Assembly at United Nations headquarters in New York, New York, USA, on 21 September 2011. Media reports state on 31 December 2011 that President Goodluck Jonathan has declared a state of emergency in areas affected by attacks from the Islamist group Boko Haram. Borders will be temporarily closed in the north-eastern states of Yobe and Borno, and central state of Plateau. EPA/JASON SZENES *** Local Caption *** 00000402928322 +++(c) dpa - Bildfunk+++
Hoto: picture-alliance/dpa

A baya dai ya ciza ya kuma tauna da nufin kawo ƙarshen abun da gwamnatin ta kira ta'addanci irin na 'ya'yan ƙungiyar Boko Haram. Kai har ma an kai ga saka wa'adi na watan Yunin da muke ciki domin adabo da annobar da ta shafi sarki da talakan cikin ƙasar ta Najeriya.

To sai dai kuma daga dukkan alamu dabara tana shirin ƙare wa shugaban Najeriya Goodluck Jonathan da a karon farko ya fito ya amince da irin girman ƙalubalen dake gabansa a yaƙin.

Burin 'yan ta'adda shi ne durƙusar da gwamnati

Jonathan ɗin da ya share tsawon awoyi har biyu yana amsa tambayoyin 'yan jarida dai ya ce babban burin ƙungiyar na zaman durƙusar da gwamantinsa ko ta halin ƙaƙa. Abun da kuma a cewar shugaban ke zaman ummul aba'isin kai hare hare kan coci coci a sassa daban daban na arewacin tarrayar ta Najeriya.

"In ka kalle ɓulla da girman ƙungiyar ta Boko Haram za ka ga akwai sauyin taku da rawa. Kuma sha'awar duk wani dan ta'adda shine rusa gwamanti, in wata dabara ba ta yi aiki ba sai su sauya wata. Shi yasa muma muke sauyawa muna tunanin ya kamata wasu ma su ɗana domin ganin irin sauyin da za mu samu. Ba wai wanda suke nan basu yi ƙoƙari ba. Za mu ci-gaba da sauya tsarin tsaronmu in kuma ta kama da mutanen dake tafi da shi."

Tuni dai shugaban ya sake miƙa goron gayyata ga 'ya'yan ƙungiyar da a baya gwamnatin ta ce ba ta da niyyar tattauna ta'addancin su akan tebur. Tare kuma da tayin ahuwa ga waɗanda suka amince su ajiye makamansu cikin yaƙin.

ARCHIV - Ein Nigerianischer Soldat steht neben einem Motorradfahrer an einem Militär-Checkpoint in Kano, im Norden von Nigeria, am 21 Januar 2012. Am 20. Januar 2012 verübte die islamistischen Sekte Boko Haram in Kano eine Serie von Anschlägen, bei der fast 200 Menschen starben. Die Metropole gilt als sehr gefährlich für westliche Ausländer. Ein in Nigeria entführter Deutscher ist nach Informationen der Zeitung «Daily Trust» von seinen Kidnappern getötet worden. Der Mann, der für die Firma Bilfinger Berger arbeitete, war Ende Januar in der Millionenstadt Kano im Norden des Landes verschleppt worden. Die Geiselnehmer hätten den Entführten erschossen, als sie von einem geplanten Befreiungsversuch der Armee gehört hätten, berichtete die nigerianische Zeitung am Donnerstag (31.05.2012). EPA/STR
Tsaurara matakan tsaro bai canza komai baHoto: picture-alliance/dpa

Sababbin matakan kuma dake zaman na baya baya a yaƙin da ya kai ga hallaka mutane kusan 1000 a farkon watanni shida na wannan shekara da muke ciki kaɗai.

Matakan kuma da daga dukkan alamu suka gaza burge 'yan ƙasar ta Najeriya da ke yi wa gwamnatin kallon wadda ta kasa fahimtar 'ya'yan ƙungiyar har ya zuwa yanzu.

Dr. Usman Mohammed dai na zaman wani mai sharhi kan harkokin siyasa da ma rigingimun a Najeriya.

Harin bom ya zama ruwan dare a arewacin Najeriya

Rashin sanin da ya ɗara dare duhu ko kuma kau da ido don son ra'ayi dai, duk da sababbin matakan na gwamnati dai ana shirin ƙare watan na Yuni tare da ƙara ta'azzarar boma bomai da ragowar hare haren da ya zuwa yanzu suka koma ruwan dare gama duniyar arewacin ƙasar ta Najeriya.

Abun kuma da a cewar Senator Lawali Shu'aibu dake zaman sakataren jam'iyyar CAN ta 'yan adawar ƙasar ya sanya mantawa da karatun makomar ƙasar zama na 'yan PDP da 'yan garin mu zama wajibi a ɓangaren mahukuntan dake jagorantar harkokin ƙasar ta Najeriya a yanzu haka.

epa03095737 Nigerian boys sift through the remains of the Gamboru market after multiple explosions in Maiduguri, northern Nigeria, 07 February 2012. Three people have died in bomb blasts by the radical Islamist group Boko Haram in northern Nigeria, police said 07 February. Police told the German news agengy dpa that the owner of a pharmacy in the northeastern city of Maiduguri, and two of his employees, were killed when bombs went off. In the city of Kano, two police stations where Boko Haram members were being detained were also targeted. Police said there were no deaths. Boko Haram claimed responsibility for both attacks, which occurred as residents were observing Eid-el-Mulud, the Muslim festival marking the birth of the Prophet Mohammed. In the nearby town of Kaduna a man in military uniform was reported to have blew himself up outside an army barracks. Boko Haram Islamist militants have recently killed hundreds in bomb attacks across northern Nigeria. EPA/STR
Hoto: picture-alliance/dpa

Abun jira a gani dai na zaman makomar rikicin da ma tayin gwamnatin da sau biyu ake batun tattaunawa, sau biyun kuma ana rushewa a cikin tsawon watanni uku.

Mawallafi: Ubale Musa
Edita: Mohammad Nasiru Awal