1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Binciken ICC kan rikicin Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya

February 7, 2014

Babbar mai gabatar da kara ta kotun ICC da ke hukunta manyan laifun yaki ta ce sun kaddamar da bincike a Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya don duba ko an aikata laifukan yaki.

https://p.dw.com/p/1B5HV
Babbar mai gabatar da kara ta kotun ICC Fatou BensoudaHoto: Reuters

Bensouda ta ambata hakan ne a wannan Juma'ar inda ta ce sun yanke shawarar fara binciken ne saboda halin da ake ciki musamman ma dai kashe-kashe da kuma wasu batutuwa na tauye hakkin bani adama a kasar sun wuce gona da iri.

Babbar mai gabatar da karar ta ce wani abu da ya zaburar da su wajen yin bincike shi ne irin rahotannin da suka samu dangane da irin cin zarafin jama'a da kungiyoyi daban-daban ke yi a kasar tun da aka fara rikici mai nasaba da kabilanci da addini a kasar a watannin da suka gabata.

Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Pinado Abdu Waba