1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Bin Salman: Mun karya karfin Iran a Afirka

Mahmud Yaya Azare AS
April 24, 2018

Ana ci gaba da samun cece-kuce kan jawabin da yarima mai jiran gadon mulkin Saudiyya Muhammad Bin Salman ya yi kan cewa kasarsa ta yi nasarar karya tasirin da Iran da kawayenta ke da shi a Afirka.

https://p.dw.com/p/2waAi
Saudi-Arabien | Kronprinz Mohammed bin Salman
Hoto: picture alliance /dpa/Saudi Press Agency

A wata hira da jaridar Times ta Amirka ta yi da yarima mai jiran gadon na Saudiya Muhammad Bin Salman ya ce kasarsa ta kai gouro ta kai mari a Afirka don ganin ta rage tasirin Iran a nahiyar, yadda ya zuwa yanzu tai nasarar karya karfin kasar ta Iran a Afirka da kimanin kaso 95 cikin 100.

Nigeria Demo für die Freilassung von Ibraheem Zakzaky
Muhammad Bin Salman ya ce kasarsa ce ta dakushe karfin Ibrahim al-Zakzaky a NajeriyaHoto: picture alliance/AP Photo/Sunday Alamba

Dr Zayeed Al-Amri mamba a cibiyar tsara dabarun mulki da tunkarar matsaloli na kasar ta Saudiya ya yi karin bayani kan manufar yariman inda ya ke cewar "abun da yarima ke nufi a nan shi ne tun bayan da ya ayyana shirinsa na tunkarar makiya mai suna Saudiya tai nasarar karya tanadin Iran a Yemen da Somaliya da Djibouti da Sudan kamar yadda ta lalata yunkurinta na kafa makamanciyar kungiyar Hizbollah a Nigeriya da hana Ibrahim Zakzaky yin juyin mulki a kasar''.

To sai dai duk da hakan, wasu na ganin kasar ta Saudiya na yin azarbabi da zuga kanta fiye da kima kan ikirarin da ta ke na karya karfin kasar ta Iran a Afirka yadda a daidai lokacin da Bin Salman din da ke tsuke bakin ajjihu ya ke rage kudaden hanayen jari a Afirka ya ke kuma  ayyana yaki kan yada akidar Wahabiyanci sai dai kasar ta Iran a hanu guda na kara matsa kaimi wajen kulla sabin huldodin da Afirkan gami da bada guraban karatun ilimin kimiya da fasaha ga daliban na Afirka yadda a yanzu haka ministan harkokin wajen Iran Muhammad Javad Zareef  ya isa kasar Senegal a rangadin da ya ke a kasashen Afirka.

Mohammad Javad Zarif iranischer Außenminister
Ministan harkokin wajen Iran da ke ziyara a Afirka na kokari wajen kulla kawance da wasu kasashen AfirkaHoto: Getty Images/AFP/A. Kenare

Hakan dai ya sanya Dr. Amani al-Taweel ta cibiyar bincike Al-Ahram a Masar nuna takaicinta na yadda kasashen biyu ke rura wutar rikicin addini a Afirka don cimma muradunsu na mamaya a yanki. Dr. al-Taweel ta ce "a gaskiya Saudiya ba abun da ya fi damunta tamkar yada akidar Wahabiyanci a Afirka fiye da kulla huldar kasuwanci da alakar diflomasiyya ta ban gishiri in baka manda''.

Manazarta dai na ganin cewa muddin kasashen Afirka basu raba lamuran addini da na siyasa ko diflomasiyya a alakarsu da kasashen na Saudiya da Iran  ba to ko shakka babu kokawar yin babakeren da kasashen ke yi da sunan addini kan iya kaiwa Nahiyar ta Afirka ya baro wacca dama can ta ke fama da rikice-rikicen kabilanci da kalubalen talauci da cutattuka.