1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Biden ya tattauna da shugabannin Turai

November 11, 2020

Zababben shugaban Amirka Joe Biden ya tattauna da shugabannin kasashen Turai aminan Amirka da suka hada da Firaministan Birtaniya Boris Johnson da shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel da kuma shugaba Macron na Faransa.

https://p.dw.com/p/3l7lk
Frankreich Biarritz 2019 | Boris Johnson, Angela Merkel & Emmanuel Macron
Hoto: Getty Images/A. Parsons

Manyan shugabannin kasashen duniya aminan Amirka sun tattauna ta wayar da tarho da zababben shugaban kasar Joe Biden inda suka jaddada aniyarsu ta hada hannu domin aiki tare, duk kuwa da ikirarin da sakataren harkokin wajen Amirka Mike Pompeo yake yi na cewa shugaba Trump ne zai cigaba da jagorancin kasar. 

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Markel ta wayar tarho, ta bi sahun kasashen duniyar wajen taya Joe Biden murnar nasarar da ya samu.

Mai magana da yawun shugabar Steffen Seibert ya ce shuwagabannin guda biyu sun tattauna batun kawance tsakanin Turai da Amirikar. 

Kasashe da dama na tarayyar Turai sun baiyana fatan kyautatuwar dangantaka tsakanin tarayyar Turai da Amirka a karkashin mulkin Joe Biden.