1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zanga-zangar adawa da gwamnati a Bangladesh

August 2, 2024

A kalla mutane 20 ne suka jikkata a arangama tsakanin masu zanga-zanga da jami'an tsaro a Bangladesh, yayin da jama'a ke boren nuna kin jinin gwamnatin Firanminista Hasina.

https://p.dw.com/p/4j3eN
Dubban al'ummar Bangladesh na neman Firanminista Hasina ta yi murabus
Dubban al'ummar Bangladesh na neman Firanminista Hasina ta yi murabusHoto: DW

Masu boren dai na neman firanminista Bangladesh, Hasina ta sauka daga mukaminta tare da neman 'yanci ga iyalan mutum 150 da aka kashe lokacin zanga-zanga dalibai kan tsarin daukan aiki a kasar. An ruwaito cewa, jami'an 'yansanda sun tarwatsa masu zanga-zangar da hayaki mai sa hawaye da kuma harsashen roba a arewa maso gabashin garin Habibganj.

Karin bayani: Daliban Bangladesh sun sha alwashin ci gaba da zanga-zanga

Rikicin da kasar ta fada a wannan lokacin shi ne bore mafi girma da gwamnatin Hasina ke fuskanta, bayan wata zanga-zangar da aka yi a lokacin da ta yi tazarce a karo na hudu a kan karagar mulkin kasar, sakamakon lashe zaben watan Janairun 2024 da 'yan adawa suka kauracewa.