1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Bacin ran kasashe kan harin Birtaniya

March 23, 2017

Yayinda ake ci-gaba da binciken musabbabin harin, hukumomin London sun tsare mutane da yawa, haka kuma kasashen duniya na aika sakonnin jajantawa kasar bayan kai hari a majalisar dokoki a tsakiyar wuraren yawon shakatawa

https://p.dw.com/p/2ZmxV
Großbritannien Terroranschlag in London | Whitehall, Polizei am Tag danach
Hoto: picture-alliance/dpa/J. Brady

Shugabannin kasashen duniya na ci gaba da bayyana takaici kan harin majalisar dokokin Birtabiya da wani ya kai a jiya Laraba, tare da yin Allah wadai da lamarin.

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel, ta ce Jamus da al'umarta baki daya na tare da Birtaniya a yaki da ayyukan ta'addanci ta ko wane fanni. Haka Shugaban Jamus Frank-Walter Steinmeier ya ce manufar Jamus guda ce da Birtaniyar a yaki da ta'addancin.

Jami'an ‘yan sandan birnin London sun ce suna da bayanai kan mutumin da ya kai harin a jiya Laraba wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 5 tare da jikkatar wasu sama da 40.

Mutumin dai ya kutsa cikin mutane da mota, a kan gadar Westminster inda masu tafiya a kasa suke, kafin daga bisani ya gangara zuwa majalisar dokokin kasar da ke a birnin na London.

Sai dai fa jami'an 'yan sandan ba su bayar da karin bayani kan mutumin da ya kai harin ba.