1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Babban taron duniya a birnin Paris kan makomar Libiya

September 1, 2011

Tun gabanin taron tarayyar Turai ta ɗage wani kaso na takunkuman da ta sanya wa gwamnatin Gaddafi.

https://p.dw.com/p/12Rfi
Shugaban Faransa Nicolas Sarkozy ke ɗaukar nauyin taro kan makomar LibiyaHoto: picture-alliance/dpa

Jami'ar kula da harkokin wajen EU Catherine Ashton wadda ta ba da sanarwar ɗage takunkuman a birnin Brussels ta ce an janye haramci da aka sanya wa kamfanonin da hukumomin Libiya guda 28, ciki har da bankuna da kamfanonin mai da na isakar gas. A Jamus kaɗai an ƙiyasta cewa kadarorin Libiya dake cikin ƙasar sun kai na Euro miliyan dubu 7.3, a saboda haka ministan harkokin wajen Jamus Guido Westerwelle yayi kira da a gaggauta sakin waɗannan kuɗaɗe domin taimakawa al'umomin Libiya.

"Libiya ƙasa ce mai ɗinbim arziki da ya wuce misali musamman na makamashi. Saboda haka ya kamata a ɗage wannan takunkumin da aka ɗaro wa gwamnatin Gaddafi, domin taimakawa a fannonin kiwon lafiya da samar da abinci da sake gina wasu ɓangarorin ƙasar da aka lalata."

Sa'o'i ƙalilan gabanin buɗe babban taron duniya kan ƙasar ta Libiya a birnin Paris na ƙasar Faransa, Rasha mai ikon hawa kujerar naƙi a Majalisar Ɗinkin Duniya ta amince da majalisar wucin gadin 'yan tawayen Libiya a matsayin halastacciyar wakiliyar ƙasar.

Shugaban Faransa wanda ya kira taron na Paris a wannan Alhamis, ya jaddada rawar da ƙasarsa da kuma Birtaniya suka taka a matakan sojin da ƙungiyar NATO ta ɗauka kan Libiya.

"A karon farko tun bayan shekarar 1949, NATO ta tafiyar da aiki a matsayin wata ƙungiyar ƙawance wadda ƙasashen Turai guda biyu wato Birtaniya da Faransa suka jagoranta."

Shugaban na Faransa ya jawo hankali cewa tun farko Amirka ba ta yi niyar shiga a dama da ita sosai a Libiya ba.

Mawallafi: Mohammad Nasiru Awal
Edita: Umaru Aliyu