1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana zaman dar-dar tsakanin Indiya da Pakistan

Usman ShehuJanuary 8, 2013

Hankula sun tashi a kan iyakar Indiya da Pakistan, inda aka yi musayar wuta da ta haddasa mutuwa daga bangarorin biyu

https://p.dw.com/p/17GCr
Pakistan President Asif Ali Zardari, left, talks with Indian Prime Minister Manmohan Singh during their meeting at the latter's residence in New Delhi, India, Sunday, April 8, 2012. Zardari arrived in India on a private trip Sunday that also gives him a chance to meet Indian leaders amid a thaw in relations between the two South Asian rivals. (AP Photo/Prakash Singh, Pool)
Shugaban Pakistan Asif Ali a ganawarsa da firimiyan Indiya Manmohan SinghHoto: AP

Hukumomin soji a kasar Indiya suka ce, an hallaka sojojinsu biyu, a wani musayar wuta da aka yi da wasu mutane dauke da makamai, a kan iyakar kasar da Pakistana, bangaren yankin Kashmir da ke samun takaddama tsakanin Pakistan da Indiya. Kakakin sojan Indiya a yankin yace, sojan kasar dake sintiri sun hangi gungun wasu mutane na kaikawo a kan iyakar ta su, bayan da sojan kasar suka nemi mutanen su yi surenda, sai kawai suka bude wa sojan wuta. Hatsarin yazo ne kwana biyu bayan da Pakistan tace soajan Indiya da suka getara kan iyakar da suke takaddama, sun hallaka sojan Pakistan daya. A wannan yankin da kasashen biyu da suka mallaki makamin nukiliya ke gardama a kansa, ana yawan samun hari kan juna, ko da yake yan shekarunnan dangantaka tsakanin kasashen biyu ta inganta. Gwamnatin Pakistan dai tuni ta musanta hannunta a harin da Indiya tace Pakistan ke da alhaki.

Mawallafi: Usman Shehu Usman

Edita: Mohammed Nasir Awal