1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana shiga yajin aiki a Sudan

May 28, 2019

Rahotannin da ke fitowa daga Sudan, na cewa an shiga yajin aikin kwanaki biyu a kasar wanda masu zanga-zanga suka kira. Sudan ta fada rikicin siyasa bayan hambare Shugaba al Abashir.

https://p.dw.com/p/3JGaz
Sudan Streik in Khartoum
Hoto: picture-alliance/AP Photo

Hakan dai wani kokari ne na ci gaba da matsa wa sojojin kasar lamba don ganin sun mika mulki ga gwamnatin farar hula.

Sojojin kasar da suka karbe mulki daga hannun tsohon Shugaba Omar al Bashir cikin watan jiya, sun gaza cimma matsaya da jagororin kungiyoyin fararen hula kan yadda za a sama wa kasar alkibla.

Jagororin zanga-zangar sun ce yajin aikin zai hada da likitoci da alkalai da lauyoyi da ma'aikatan ruwa da wuta.

Haka ma abin yake ga bangaren sufurin jiragen sama da na kasa da ma bangaren sadarwa.

Kafin wannan matakin dai, an ga shugabannin gwamnatin kasar na ziyarce-ziyarcen kulla alaka da wasu kasashen larabawa.