1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana gudanar da bincike a Siriya

July 15, 2012

Tawagar masu saka ido na Majalisar Ɗinkin Duniya(MDD) da ta kai ziyara a garin Tremseh ta ce an kai hare hare a gidajen waɗanda suka canza sheƙa

https://p.dw.com/p/15XyD
A view shows damaged buildings in the old city of Homs April 3, 2012. Picture taken April 3, 2012. REUTERS/Karam Abu Rabeh/Shaam News Network/Handout (SYRIA - Tags: CIVIL UNREST) FOR EDITORIAL USE ONLY. NOT FOR SALE FOR MARKETING OR ADVERTISING CAMPAIGNS. THIS IMAGE HAS BEEN SUPPLIED BY A THIRD PARTY. IT IS DISTRIBUTED, EXACTLY AS RECEIVED BY REUTERS, AS A SERVICE TO CLIENTS
Syrien Zerstörung April 2012Hoto: Reuters

A cikin wata sanarwa da ya baiyana wani mai magana da yawun tawagar ya ce sun ga gidaje da makarantu da aka ƙone ƙurmus, sannan kuma jini na zube barjat koi'na a cikin gidajen.'Yan adawar na Siriya sun ce mutane sama da ɗari biyu suka rasa rayukansu a cikin farmakin, to amma tawagar ba ta tabbatar da addadin ba. Sai dai ta ce sojojin gwamnatin sun yi amfanin da muggan makamai.

Ƙasashen Jamus da Ingila da Amirka da Faransa da Portugal sun gabatar da wani ƙudirin doka ga MDD, wanda ke bai wa shugaba Assad wa'adin ƙwanaki goma na ya dakatar da yin amfani da manyan makama, wajan kai hare hare akan al' ummarsa, ko kuma ya fuskanci ƙarin takunkumi.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Halima Balaraba Abbas