1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana fargabar aukuwar bala'in aman wuta

Ramatu Garba Baba
November 27, 2017

Gwamnatin kasar Indonesiya ta nuna damuwa kan bayyanar alamun bala'in aman wuta a tsibirin yankin Bali inda yanzu ta bayar da umurni na kwashe dubban mutane don kare rayuwarsu.

https://p.dw.com/p/2oMOb
Indonesien Bali Ausbruch des Vulkans Mount Agung
Hoto: Reuters/Antara/N. Budhiana

An dauki matakin kwashe dubban mutane daga wasu wuraren da ke kan hadarin fuskantar bala'in a wannan Litinin. Wuraren da matsalar ta shafa sun hada har da babban filin jirgin yankin da ke da dubban matafiya.Alamun aman na wuta sun bayyana ne a makon da ya gabata, lokacin da aka ga wani hayakin da ke nuna yi yuwar bala'in ya tirnike wani tsauni mai nisan sama da kilomita 3 zuwa sararin samaniya.

Fargabar ta tilastawa hukumomi dakatar da zirga-zirgar jirage a yankin tsibirin na Bali. Mutane sama da dubu 40 da ake ganin lamarin zai iya shafa sun kauracewa yankin, yayin da a bangare guda hukumomin kasar ta Indonesiya suka yi shelar kwashe wasu karin mutum dubu 100 da ka iya shiga cikin wannan hatsari.