1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana ci-gaba da zakulo mutane bayan girgizar kasa a China

September 8, 2012

A kalla mutane 80 ne suka rasa rayukansu yayin da sama da 100 suka bace a girgizar kasar da ta wakana a kasar China

https://p.dw.com/p/165MA
A collapsed house is seen after two earthquakes in Zhaotong, Yunnan province, September 7, 2012. Two shallow 5.6 magnitude earthquakes hit southwestern China on Friday, killing at least 50 people and forcing tens of thousands of people from damaged buildings, state media said. REUTERS/Stringer (CHINA - Tags: DISASTER ENVIRONMENT) CHINA OUT. NO COMMERCIAL OR EDITORIAL SALES IN CHINA
Hoto: Reuters

Rahotannin baya bayan nan sun tabbatar da mutuwar a kalla mutane 80 sakamakona wata gigizar kasar da ta faru a kasar Sin ko kuma China a karshen makon nan. Wata girgizar kasa mai karfin marki 7 da digo 6 ta kacancana wasu yankunan kudanci da yammacin kasar inda yanzu haka masu ayyukan ceto ke ci-gaba da binciken tsammanin warabbuka domin zakulo wasu mutanen da a ke saran sun bata. Yankunan kasar ta Sin ko kuma China na fuskantar yawan girgizar kasa inda ko a shekarar da ta gabata sama da mutane dubu 3 ne suka rasa rayukansu a makamantan wadannan haduran. Wannan al'amarin ya zo ne bayan rugujewar wata mahakar ma'adanai a arewacin kasar inda a kalla mutane 107 ne suka rasa rayukansu.

Mawallafi: Issoufou Mamane
Edita : Saleh Umar Saleh