1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Adadin wadanda suka rasu sun karu a Turkiyya da Siriya

Abdoulaye Mamane Amadou ATB
February 13, 2023

A yayin da masu aikion ceto ke fitar da tsammanin kan ragowar masu sauran numfashi a baraguzan gine-gine a Turkiyya da Siriya, adadin wadanda suka rasu na dada karuwa.

https://p.dw.com/p/4NQ5F
Yadda Iftila'in girgizar kasa a ya ruguza gidaje a Turkiyya
Yadda Iftila'in girgizar kasa a ya ruguza gidaje a TurkiyyaHoto: Kyodo/picture alliance

Turkiyya za ta kai karar wasu kamfanonin gine-ginen kasar da ta zarga da sakaci wajen kara ta'azzara mummunar girgizar kasar da ta yi mummunan illa.

Mataimakin shugaban Turkiyya Fuat Oktay, ya bayyana cewa akwai akalla kamfanoni 130 da ke shirin shiga komar mahukunta kan zarginsu da rashin samar da gine-gine mafi inganci a wurare da dama.

Ya zuwa wannan Litinin, akalla mutane dubu 35 ne suka rasu sakamakon tagwayen bala'o'in a Turkiyya da Siriya, adadin da kuma masu ceto ke ittifakin cewa ka iya karuwa nan da wasu lokutta.

Duk da debe tsammanin da ake na samun ragowar masu sauran numfashi, an ceto wasu mutane hudu a jiya Lahadi da ransu.