1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana ci gaba da yin luguden wuta a Siriya

July 30, 2012

Rahotanin da ke karo da juna a fadan da dakarun gwamnatin da na yan tawaye suke gwabzawa a birnin Aleppo na kasar Siriya na cewar ko wane na iƙirarin samun galaba

https://p.dw.com/p/15gqK
A Free Syrian Army member takes position while people flee after hearing shelling at Aleppo's disctrict of al- Sukkari July 29,2012. REUTERS/Zohra Bensemra (SYRIA - Tags: POLITICS CIVIL UNREST MILITARY )
Hoto: Reuters

Tun da farko dai dakarun gwamnatin sun sanar sun karpe iko da wani ɓangare na unguwar Salahedine amma kuma daga bisanni yan tawayen suka musunta ikirarin.

sannan kuma yan tawyen sun ce su ƙwace garin Denadem da ke kan iyaka da Turkiya abinda zai ba su damar shigo da makamai;ministan harkokin waje na faransa ya ce ƙasarsa za ta kira wani taro na musammun.''ya ce tun da Faransa zata karɓi  ragamar kwamitin sulhu na Majalisar Ɗinkin Duniya a cikin watan Augusta mai shirin kamawa;ya ce zamu kira wani taron gaggawa na ministocin harkokin waje kafin ƙarshen wannan mako.

Rahotannin da ke zuwa mana y kuma ,na cewar babban sakataran MDD Ban Ki Moon  ya sanar da cewar  dakarun gwamnati na Siriya sun kai farmaki  ga tawagar Majalisar mai saka ido a ciki hada shugaba tawagar sai dai sanarwa ta ce babu  wanda ya samu rauni a cikin su.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane

Edita       : Mohammed Nasir Auwal