1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An ɗage tattaunawar sulhun Sudan ta Kudu

February 10, 2014

A wannan litinin ne aka sa ran gudanar da tattaunawar sulhu tsakanin ɓangarorin dake gaba da juna a Kudancin Sudan amma kuma an ɗage zuwa wani lokaci da za a sanar

https://p.dw.com/p/1B6CK
Südsudans Präsident Salva Kiir Mayardit
Salva Kiir, Shugaban ƙasar Sudan ta KuduHoto: Reuters

Jami'ai a Addis Ababa na ƙasar Ethiopiya sun ce an ɗage tattaunawar sulhun da aka shirya gudanarwa a wannan litinin tsakanin ɓangarorin dake yaƙi da juna a Kudancin Sudan bayan da aka shafe makonni biyu da ƙulla yarjejeniyar tsagaita wutar da ba ta ɗore ba.

To sai dai tun da fari, Ambassador Mahboub Ma'alim wanda ke zaman babban sakataren ƙungiyar dake raya tattalin arziƙin ƙasashen yankin gabashin Afirka wato IGAD ya faɗawa gidan talibijin na Ethiopiyar cewa a wannan karon tattaunawar za ta mayar da hankali ne kan yin sulhu a siyasance da sasanta tsakanin 'yan ƙasa.

A watan Disemban bara ne yaƙi ya ɓarke tsakanin dakarun dake biyayya ga gwamnati da kuma waɗanda ke biyayya ga tsohon mataimakin shugaban ƙasa Reik Machar, wanda yayi sanadiyyar ƙauracewar dubban 'yan ƙasa, domin tsira da rayuwarsu.

Kawo yanzu dai an dai sakar wa gwamnatin Kenya wasu fursunonin siyasa dake biyayya ga tsohon mataimakin shugaban ƙasar Reik Machar, amma ba a kai ga sannin ko za su kasance a tattaunawar sulhun ba.

Mawallafiya: Pinaɗo Abdu Waba
Edita: Muhammad Nasiru Awal