1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An yanke hukuncin kisa ga wasu fursuna a Masar

Abdourahamane HassaneFebruary 2, 2015

Kotun ɗaukaka ƙara ta ƙasar ta tabbatar da hukuncin kisa ga wasu mutane 183 magoya bayan tsohon shugaban ƙasar Mohammed Morsi.

https://p.dw.com/p/1EUS3
Ägypten Ausweisung Journalist Peter Greste ARCHIVBILD 2014
Hoto: Khaled Desouki/AFP/Getty Images

Kotun ta ce ta samu mutanen da laifin taka rawa a lokacin da masu bore suka kashe wasu 'yan sanda guda 11 da wasu farar hula guda biyu,a Kerdassa da ke a yammacin birnin Alƙahira a cikin watan Augusta na shekara ta 2013.

A lokacin zanga-zanga da ta yi sanadiyyar kifar da gwamnatin Mohammed Morsi a cikin watan Yuli na shekarar ta 2013. A halin da ake ciki kuma wata kotun a ƙasar ta Masar ta sanar da cewar nan gaba a ranar 15 ga wannan wata. Za a sake gurfanar da tsohon shugaban ƙasar Mohammed Morsi a gaban ƙuliya a karo na fuɗu a kan laifin cin amanar ƙasa da kuma leƙen asiri.