1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Kamaru: 'Yan gudun hijira 18 sun mutu a harin ta'addanci

Ramatu Garba Baba
August 5, 2020

An tura wata tawaga ta jami'an aikin ceto zuwa wani sansanin 'yan gudun hijira da ke arewacin kasar Kamaru, bayan wani hari da ake zargin na ta'addanci ne da ya yi sanadiyar rayukan 'yan gudun hijira kimanin 18.

https://p.dw.com/p/3gQaU
Zentralafrikanische Flüchtlinge sammeln sich im Camp
Hoto: Kouam Joel Honore

An tura wata tawaga ta jami'an aikin ceto zuwa wani sansanin 'yan gudun hijira da ke Arewacin kasar Kamaru, bayan wani hari da aka kai da ya yi sanadiyyar rayukan 'yan gudun hijira kimanin 18.

Wani mai magana da yawun Hukumar kula da 'yan gudin hijira ta Majalisar Dinkin Duniya (UNHCR) Babar Baloch, ya fada ma taron manema labarai a birnin Geneva cewa, hukumar na zargin mayakan Boko Haram da hannu a harin na ranar Lahadin da ta gabata.

Jami'in ya kara da cewa, tun daga watan Yuli, ake samun karuwar hare-hare daga mayakan kungiyar ta Boko Haram da wasu kungiyoyi na masu gwagwarmaya da makamai a yankin da ke iyaka da tarayyar Najeriya.