An sake sallamar wani hafsan sojin ƙasar Jamus
March 13, 2010Talla
Ta bayyana cewa ministan tsaron ƙasar Jamus Karl-Theodor
zu Guttenberg ya sake sallamar wani hafsan sojin ƙasar, a wani abinda ya shafi harin da sojojin ƙasar Jamus suka
bayar da umarnin kaiwa a yankin Kunduz na ƙasar Afganistan,
kuma ya hallaka jama'a da yawa. Ma'aikatar tsaron ƙasar
ta tabbatar ta da cewa an sallami Birgediya Janar
Henning Hars daga aiki. Janar Hars wanda tsohon
jami'in tarone a offishin jakadancin Jamus dake a birnin Washington na Amirka
ya rubutawa ministan tsaron Jamus wasiƙa, inda ya yi
suka bisa sallamar man'yan hafsoshin soji na ƙasar da aka yi. Janar ɗin ya kuma buƙaci ministan da ya sake duba batun harin na watan satumban bara wanda ya hallaka 'yan
Afganistan142 akasari fararen hula.
Mawallafi: Usman Sheh Usman