1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kai hare-hare a cocinan Kaduna

June 17, 2012

Mutane fiye da 20 su ka rasa rayuka a wasu jerin hare-haren da suka rutsa da wuraren ibadan kirista a jihar Kaduna

https://p.dw.com/p/15GoY
epa03026909 Nigerian police control a street shortly after a bomb blast in a market in Ogbomoshoin area of Kaduna, Nigeria, 07 December 2011. Reports state the early morning explosion in the northern city of Kaduna killed 10 people, including a pregnant woman and two children. A group suspected to be Islamist militants reportedly arrived on motorbikes and threw bombs into the crowded spare parts market. EPA/STR +++(c) dpa - Bildfunk+++
Hoto: picture-alliance/dpa

Mutane fiye da 20 suka rasa rayuka, sannan kimanin wasu 100 su ka ji raunuka, a cikin wasu tagwayen hare-haren ƙunar baƙin wake a cocinan biranen Kaduna da Zariya dake arewacin tarayya Najeriya.

Har yanzu dai babu ƙungiyar da ta ɗauki alhakin kai wannan hari, amma makon da ya gabata,ƙungiyar Boko Haram ta yi shelar ɗaukar alhakin kai hare-hare masu kama da wannan a daidai lokacin da mabiya addinan kirista ke aiyukan ibada.

Jim kaɗan bayan kai hare-haren, matasan kirsitoci sun fito a tinuna domin nuna ɓacin rai.

A wani mataki na riga kafin bazuwar tashe-tashen hankula, gwamnatin jihar Kaduna ta kafa dokar ta ɓacin sa' o' i 24.

Mawallafi:Yahouza Sadissou Madobi
Edita: Umaru Aliyu