1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kafa gwamnatin rikon kwarya a Libiya

February 5, 2021

Bangarorin da basa ga maciji da juna na Libiya sun zabi sabuwar hukumar wucin gadi da za ta jagoranci shirya zaben gama gari a kasar a watan Disamban shekarar 2021.

https://p.dw.com/p/3oy10
Schweiz Libysches Dialogforum in Genf
Hoto: UNITED NATIONS/AFP

An dai zabi Muhammad Yunus Al-manfy a matsayin Shugaban majalisar zartarwa na gwamnatin rikon kwaryar yayin da aka zabi Abdulhameed Dabeebah a matsayin sabon firanminista.

Wannan zaben dai ya kawo karshen mulkin tsofin jami'an gwamnatin hadakar kasar da ta kunshi Aqilah Saleh, shugaban majalisar Gabashin kasar, da Fathy Bashaga, ministan cikin gidan gwamnatin Tripoli wadanda suka sha kaye a zaben.